Shugaban ‘Yan Sanda Ya Nemi Kotu Ta Janye Hukuncin Daurin Da Ta Yi Mishi

Sufeto Janar na ‘Yan Sandan Najeriya IGP Usman Alkali Baba ya shigar da ?udirin neman jingine umarnin kotu da ya ?aure shi wata uku a gidan yari, yana mai cewa bai raina umarnin kotun ba.

Cikin ?orafin da ya gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja ranar Alhamis, shugaban ‘yan sandan ya ce ba a ?ar?ashin shugabancinsa aka aikata laifin da kotun ta yi hukunci a kansa ba kuma “ba a sa?a wa umarnin kotu ba”.

A makon nan ne Babbar Kotun Tarayya ta ba da umarnin kama babban sufeton tare da gar?ame shi tsawon wata uku saboda sa?a umarnin kotun da ta ce a mayar da Patrick C. Okoli kan aikinsa bayan an tilasta masa yin ritaya ba bisa ?a’ida ba.

“Ya tabbatar da cewa an ba da umarnin ne a Nuwamban 2018 da kuma Janairun 2019 ga sufeto janar na ‘yan sanda na lokacin, ba a kansa ba wanda shi ne yake ri?e da mu?amin a yanzu,” a cewar wata sanarwa da rundunar ta fitar a yau Juma’a.

IGP Usman Baba ya ?ara da cewa sufeto janar na lokacin ya bi umarnin kotun, inda ya rubuta wasi?a ga hukumar kula da harkokin ‘ya sanda don a mayar da Mista Okoli bakin aiki.

Related posts

Leave a Comment